Show cover of Najeriya a Yau

Najeriya a Yau

Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.

Tracks

Send us Fan MailMata a Arewacin Najeriya na fuskantar kalubale da dama a fannin karantar kimiyya.  Akwai darussan da a mafi yawan lokuta ba mata kadai ba, har da mazan na kaurace musu.  Shirin Najeriya a Yau ya yi nazari  ne kan dalilan da suka sa matan Arewacin Najeriya ke tsoron karantar ilimin kimiyya.

4/14/26 • 30:00

Send us Fan MailDuk bayan shekaru hudu, Najeriya na kara yin zabe kuma ko wanne lokaci 'yan takara kan dauki alkawurika.Ko shekaru nawa wadanda ake zabe ke bukata don cika alkawuran da suka dauka?wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

4/10/26 • 30:11

Send us Fan MailAlamu na nuna cewa galibin manoma a Najeriya suna da shakku a kan amfani da irin da aka sauya ƙwayoyin halittarsa.Hakan dai na faruwa ne duk da bayanan da wasu masana suka yi game da alfanun wannan iri wanda ake kira GMO ko Genetically Modified Organism a turance.Tuni dai wasu masanan, waɗanda suka shirya wani taron bita ga manema labarai, suka yi gargaɗi game da illolin irin.Ko mece ce gaskiya game da amfani da wannan iri na GMO?

4/9/26 • 25:26

Send us Fan MailTun bayan bayyanar kirkirarrriyar basira wato AI ne dai wasu mutane suke amfani da ita ta hanyar da da bai kamata ba. Wasu sukan yi amfani da ita wajen saka hoto ko kirkirar faifan bidiyo wanda zai nuna wani yana yin abun da bai kamata ba. Hakan dai ya sa wasu suna ganin ya kamata a samar da dokokin da za su rinka lura da yadda ake amfani da kirkirarriyar basirar. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan dacewar sanya doka gane da yadda mutane za su rinka amfani da fasahar AI.

4/7/26 • 22:58

Send us Fan MailBayan hadin kai da karfafa fahimtar juna wadanda hidimar kasa take kawowa, akan samu wasu masu hidimar da sukan yi amfani da duk wata dama da suka samu don neman na sakawa a bakin salati. Yayin da wasu masu hidimar kasa sukan kama sana’a ko su saka hannun jari a inda aka tura su, wasu kuwa komawa garuruwansu suke yi bayan sun kammala. Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan irin damar da masu yi wa kasa hidima suke da ita a garuruwan da aka tura su.

4/2/26 • 22:09

Send us Fan MailSamun matasan dake bada gudunmawa a alummomin da suke rayuwa a cikin ta yana da matukar wuya a wannan zamani. Amma duk da haka, wasu matasa sun sadaukar da rayuwarsu wajen bada gudunmawarsu wajen cigaban alummarsu. Shirin Najeirya  A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan irin gudunmawar da matasa ke badawa wajen cigaban alummarsu

3/27/26 • 28:24

Send us Fan MailCin guba ta hanyar abinci (food poisoning) wata cuta ce da ke faruwa idan mutum ya ci abinci ko ya sha abin sha da ya gurɓace. Gurɓacewar abincin na iya fitowa daga ƙwayoyin cuta kamar Salmonella, E. coli, ko Listeria, ko kuma daga ƙwayoyin cutar virus, ƙwari (parasites), ko sinadarai masu guba. Alamomin cutar sun haɗa da ciwon ciki, amai, zazzabi, gudawa, da rashin jin daɗin jiki. A wasu lokuta masu tsanani, cutar na iya kai mutum asibiti ko ta yi barazana ga rayuwa, musamman ga yara ƙanana, mata masu ciki, tsofaffi, da masu raunin garkuwar jiki. wannan shine batun da shirin Najeriya  A Yau na wannan lokaci zai yi duba akai.

3/26/26 • 25:47

Send us Fan MailDuk bayan shekaru hudu, Najeriya na kara yin zabe kuma ko wanne lokaci 'yan takara kan dauki alkawurika.Ko shekaru nawa wadanda ake zabe ke bukata don cika alkawuran da suka dauka?wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

3/24/26 • 27:00

Send us Fan MailAlqurani mai girma a cikin suratul Baqarah Allah ya wajabta wa musulmi da suka cika wasu sharudda azumtar watan Ramadana.Kamar yadda malamai suka sha fadi, wannan wata na dauke da wasu falala maras misaltuwa da bawa kan samu idan ya maida kai wajen ibada don samun rabauta daga ubangiji.Kazalika hadisai sun ruwaito kan falalar azumtar kwanaki shidda na watan shawwal, watan dake biye da Ramadan.Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan falalar dake akwai ga wanda ya azumci kwanaki shidda na watan shawwal.

3/23/26 • 24:06

Send us Fan MailKo kun san sunan dabinon da kuka fi so ku ci a lokacin shan ruwa? Dan Agadas ne, ko Ruwa-Ruwa, ko Annakhiyl? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai ya yi nazari ne kan nau’ukan dabino da alfanunsa ga dan’Adam, musamman mai azumi.

3/13/26 • 30:13

Send us Fan MailShugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sha nanata muhimmancin samar da ’yan sandan jihohi a Nigeria, yana mai cewa hakan na daga cikin hanyoyin da za su taimaka wajen magance matsalolin tsaro da ke addabar sassa daban-daban na kasar. Shugaban ya bayyana cewa tsarin ’yan sanda da ke karkashin gwamnatin tarayya kadai ba zai iya biyan bukatun tsaro na kasa mai yawan jama’a da fadi kamar Najeriya ba.A wani mataki na ci gaba da duba yiwuwar aiwatar da wannan tsari, Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Tunji Disu, jim kadan bayan kama aikinsa ne ya kafa wani kwamiti na musamman domin nazartar hanyoyin da za a bi wajen samar da ’yan sandan jihohi.Sai dai duk da yadda wasu ke ganin cewa kafa ’yan sandan jihohi zai taimaka wajen inganta tsaro, masana da masu ruwa da tsaki na cewa akwai kalubale da dama da ka iya tasowa.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan irin kalubalen da shirin samar da ‘yansandan jihohi zai iya fuskanta.

3/6/26 • 25:43

Send us Fan MailA yayin da Najeriya ke fuskantar kalubale daban-daban a fannin lafiya, cutar zazzabin Lassa ta sake ɗaga kai a wasu jihohin ƙasar. Cutar wadda ake dangantawa da berayen da ke ɗauke da ƙwayar cutar, tana yawaita ne musamman a lokutan sanyi zuwa farkon damina, lamarin da ke jefa al’umma cikin fargaba a kowace shekara.Rahotanni daga hukumar dake hana yaduwar cututtuka ta Najeriya sun nuna cewa tun daga farkon shekarar 2026, an samu daruruwan mutane da suka kamu da cutar a jihohi fiye da goma sha huɗu, tare da mace-mace da dama. Jihohi irin su Bauchi State, Ondo State, Taraba State da Edo State na daga cikin wuraren da cutar ta fi yin kamari.Idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, alkaluma sun nuna cewa 2025 ta samu yawan masu kamuwa da cutar fiye da yadda aka fara gani a 2026, sai dai masana sun nuna damuwa kan yadda mace-mace ke iya ƙaruwa sakamakon jinkirin kai marasa lafiya asibiti.Shin me ke haddasa wannan yawaitar a kowace shekara? Wadanne hanyoyi za a bi wajen magance ta?Wadannan da ma wasu tambayoyin shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi kokarin amsawa.

3/5/26 • 19:44

Send us Fan MailCutar basir na daga cikin cututtukan da mutane da dama ke da mabanbantan ra’ayoyi akan ta.A lokuta da dama za ka ji yadda mutane ke fadin dalilai daban daban da ke janyo cutar basir, yayin da wasu ke ganin yawan zama ne ke kawo ta, wasu kuwa gani suke yi zaki da maiko ne ke kawo ta.Wannan shine abun da da yawa daga cikin mutane suka sani kan wannan cuta, sai dai masana kiwon lafiya na da nasu fahimtar daban kan wannan cuta.Shirin Najeriya  A Yau na wannan lokaci zai tattauna ne kan cutar basir da hanyoyin magance ta.

3/4/26 • 26:06

Send us Fan MailAlumma na yin azumi ne bisa dalilan addini don samun lada kamar yadda Allah ya umurta a cikin Qurani mai girma. Sai dai daga baya binciken masana kimiyya ya gano cewa bayan lada da ake samu daga yin azumi, akwai wasu alfanu da mai azumi ke samu ga lafiyar jikin shi da suka hada da inganta karfi da zurfin tunani zuwa fitar da gurbatattun abubuwa da jiki baya bukata. A takaice dai, ba kawai lada mai azumi ke samu ba, har da samun lafiyar jiki da na kwakwalwar sa. Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi Nazari ne kan alakar dake akwai tsakanin yin azumi da kuma lafiyar jikin mutum. 

3/3/26 • 29:58

Send us Fan MailHadisi ya tabbatar da yadda cin abinci tare yake kara dankon zumunci da kaunar juna da albarka a tsakanin al’umma. Mai yiwuwa wannan ne ya sa akan samu Karin kusanci da shakuwa a tsakanin duk iyalan da kan zauna su ci abinci. Ko kafin watan azumi dai, wasu magidantan kan mayar da cin abinci tare da tare da iyalin su al’ada. Shin ko mene ne matsayin bude-baki tare da iyali a watan Ramadana? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan irin alfanun da bude baki tare da iyali yake da shi.

2/27/26 • 26:29

Send us Fan MailShugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa sabon Sufeto Janar na ‘Yan Sanda (IGP), matakin da ya sake jawo hankalin al’umma kan makomar tsaro da gyaran harkokin rundunar ‘yan sandan ƙasar nan. Naɗin sabon jagoran rundunar ya zo ne a daidai lokacin da ake fuskantar ƙalubale daban-daban na tsaro, ciki har da satar mutane, ta’addanci, da rikice-rikicen cikin gida a wasu sassan ƙasa.Sabon Sufeton ana sa ran zai ɗora kan nasarorin da aka samu a baya tare da kawo sababbin tsare-tsare da dabarun da za su ƙarfafa yaƙi da laifuka, inganta hulɗa tsakanin ‘yan sanda da al’umma, da kuma farfaɗo da martabar rundunar. Ko ta yaya wannan naɗin sabon shugaban ‘yansandan zai amfani tsaron cikin gida Najeriya?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

2/26/26 • 18:51

Send us Fan MailRahotanni daga sassa daban-daban na siyasar Najeriya na nuna cewa ana fara samun ɓaraka a tsakanin manyan jiga-jigan haɗakar tafiyar ADC, musamman tsakanin tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi.Ko da yake har yanzu babu wata sanarwa ta hukuma da ke tabbatar da wannan saɓani, majiyoyi na nuni da cewa sabanin ra’ayi kan jagoranci, tsarin tafiya, da kuma makomar zaɓen 2027 na iya zama tushen wannan rikici.Wasu masu sharhi na ganin cewa irin wannan saɓani abu ne da kan taso a duk wata haɗaka ta siyasa, musamman idan manyan ‘yan takara masu farin jini suna ƙoƙarin haɗa kai domin cimma buri ɗaya. Sai dai tambayar ita ce: shin wannan ɓaraka za ta iya raunana haɗakar kafin ta kai ga gaci, ko kuwa za a samu sulhu a tsakaninsu?A yau, shirin Najeriya A Yau zai yi duba ne kan gaskiyar lamarin, me ke haddasa wannan jita-jita, da kuma irin tasirin da hakan zai iya yi ga makomar siyasar Najeriya.

2/24/26 • 20:11

Send us Fan MailA duk lokacin da watan azumin Ramadan ya kama, al’ummar Musulmi kan cika masallatai domin gudanar da sallar Tarawihi cikin karsashi da himma. A kwanakin farko, ana ganin sahu sun cika, zuciya cike da nishadi da kwadayin lada. Sai dai abin takaici, bayan wasu kwanaki, wasu kan fara ja da baya — wani saboda gajiya, wani saboda shagaltuwa da harkokin yau da kullum, ko kuma rashin juriya.Wannan yanayi na nuna bukatar tunatarwa kan muhimmanci da falalar sallar Tarawihi, domin ita ba kawai karin ibada ba ce a watan Ramadan, illa wata babbar hanya ce ta neman gafara da kusanci ga Allah. Manzon Allah (SAW) ya karfafa tsayuwar dare a watan Ramadan, yana mai bayyana cewa duk wanda ya tsaya sallar dare cikin imani da neman lada, za a gafarta masa zunubansa na baya.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai duba ne kan falalar sallan tarawihi yayin da Musulmi ke cigaba da gudanar da azumin watan Ramadan.

2/20/26 • 17:10

Send us Fan MailCututtuka da dama suna Kamari a Najeriya wanda a mafi yawancin lokuta ma wadanda ke dauke da irin wadannan cututtukan basu da masaniyar suna dauke da su. Kamar yadda majalisar dinkin duniya ta bayyana, zaman lafiya, rashin matsalar kwakwalwa, da samun wadata na daga cikin abubuwan dake tabbatar da lafiyar bil’adama. Wata cuta da ta addabi da yawa daga cikin al’umma itace cutar Hawan jini wacce take daya daga cututtuakan dake sanadiyyar mutuwar akalla mutum miliyan biyu a duk shekara a Najeriya.

2/19/26 • 24:51

Send us Fan MailA duk lokacin da watan azumi ya zo, Musulmai da dama sukan karɓe shi da murna da shauƙi, suna shirya ibada da ƙara kusanci da Allah. Sai dai ga wasu, musamman masu fama da larurar gyambon ciki wato ulcer, watan azumi kan zo da wani yanayi na damuwa da fargaba. Yayin da wasu ke jin daɗin azumi, su kuma suna cikin ƙalubalen yadda za su iya jure yunwa da ƙishirwa ba tare da cutar ta tashi ko ta jawo musu matsananciyar wahala ba.Ciwon ulcer na haddasa zafi a ciki, tashin zuciya, amai ko jin ƙuna musamman idan ciki babu komai na tsawon lokaci. Wannan ne ya sa azumi, wanda ke buƙatar jure yunwa daga asuba zuwa magariba, kan zama babban ƙalubale ga masu fama da wannan larura. Wasu kan kasa yin azumi gaba ɗaya, yayin da wasu ke fara shi amma su kasa kammalawa saboda tsananin ciwo.Ko ta wadanne hanyoyi ne masu fama da wannan larurar zasu bi wajen yin azumi ba tare da sun sha wahala ba?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau zai yi duba a kai.

2/17/26 • 18:14

Send us Fan Mail‘Yan kasuwa da dama a jihar Kano sun kwana sun tashi da juyayi da alhinin gobara da ta faru ta kuma lashe musu dimbin dukiyarsu suna ji suna gani ba tare da sun iya tabuka komai ba.Gobarar da ta tashi a kasuwar singa dake jihar Kano, ta fara ne da misalin karfe 4:30 na ranar asabar ta kuma cigaba da ci har zuwa wayewar garin ranar lahadi. Wannan gobara ta yi sanadiyyar raba ‘yan kasuwa da dama da hanyar cin abincin su, inda ta jefa su da iyalansu cikin halin kunci.Ko wanne irin hasara wadannan ‘yan kasuwa suka tafka sakamakon wannan gobara?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

2/16/26 • 17:21

Send us Fan MailTun bayan bayyanar kirkirarrriyar basira wato AI ne dai wasu mutane suke amfani da ita ta hanyar da da bai kamata ba. Wasu sukan yi amfani da ita wajen saka hoto ko kirkirar faifan bidiyo wanda zai nuna wani yana yin abun da bai kamata ba. Hakan dai ya sa wasu suna ganin ya kamata a samar da dokokin da za su rinka lura da yadda ake amfani da kirkirarriyar basirar. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan dacewar sanya doka game da yadda mutane za su rinka amfani da fasahar AI.

2/13/26 • 25:30

Send us Fan MailMasu iya magana kan ce banza ba ta kai zomo kasuwa. In ba haka ba, me ya kai matasan da ake zargi da aikata manyan laifuffuka ofishin ’yan sanda, suka kuma fit oba tare da wani ya harae su ko ya yi mutsu tsawa ba, balle ya saka su a cell? ’Yan sandan dai sun ce wannan wata dabara ce ta yakar aikata manyan laifuka irin su sata da fashi da makami da kwacen waya da fyade kai har ma da satar mutane don kudin fansa a tsakanin matasa.Ko yaya wannan dabara take aiki? Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari a kai.

2/12/26 • 24:44

Send us Fan MailA wannan zamani, ’yan Najeriya da dama ba sa samun wadataccen abinci a yini.Magidanta da dama, musamman, sun tsallake sun bar iyalansu sun shiga bariki don neman na sanyawa a bakin salati.  Mene ne dalilin hakan, kuma yaya za a yi a kauce wa fadawa cikin irin wannan yanayi?  Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan halin da galibin ’yan Najeriya suka tsinci kansu a ciki na rashin samun abinci yadda ya kamata 

2/10/26 • 25:59

Send us Fan MailMasu iya magana kan ce “zamani riga”.Sauyin zamani ya kawo sauye-sauye da dama a yadda ake gudanar da harkoki, ciki har da kasuwanci.A yanzu haka, zamani, intanet na taka muhimmiyar rawa wajen tallata haja ko saye da sayarwa.Shrin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan dabarun da za ku iya amfani da su don bunkasa kasuwancinku ta hanyar amfani da intanet.

2/9/26 • 27:23

Send us Fan MailA tsakanin al’ummomi daban-daban akan samu wasu al’adu na yanke wani bangare na al’aurar ’ya’ya mata saboda wasu dalilai.A kasar Hausa akan yi abin da ake kira yankan angurya da nufin rage wa mace sha’awa, musamman kafin ta yi aure.Ko menene tasirin wannan al’ada a rayuwar ’ya’ya mata?Albarkacin Ranar Yaki da Yankan Al’aurar Mata ta Duniya, shirin Najeriya  A Yau zai yi nazari a kan wannan batu.

2/6/26 • 25:44

Send us Fan MailMallakar muhalli na cikin burace-buracen kusan kowanne dan Najeriya.Sai dai wadannan burace-burace, a galibin lokuta, ba sa cika – musamman ga masu matsakaitan samu.Amma wasu masana suna ganin akwai dabarun da marasa karfi ma za su iya amfani da su don su mallaki nasu muhallin, daidai ruwa daidai tsaki.A kan wadannan dabaru shirin Najeriya A Yau zai yi nazari.. 

2/5/26 • 24:47

Send us Fan MailBabban alhakin da Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya dora wa Rundunar ’Yan Sanda shi ne kare rayuka da dukiyoyin ’yan kasa. Sai dai a lokuta da dama, akan samu fito-na-fito sakamakon zargin ’yan sanda da wuce gona da iri wajen gudanar da aiyyukan nasu.Shirin Najeriya a Yau ya tattauna a kan yadda abubuwan da ya kamata ’yan kasa su yi idan ’yan sanda suka nemi cin zalinsu.

2/3/26 • 20:08

Send us Fan MailRashin haihuwa matsala ce da ka iya wargaza gidajen aure musamman a wannan zamani.Da an samu shekara biyu zuwa uku bayan an daura aure ba tare da an samu karuwa ba za a fara yamadidi da matar a kan ba ta haihuwa.Sai dai likitoci sun ce maza ma ka iya fama da wannan larura saboda wasu dalilai.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan wadannan matsalolin da suke hana maza haihuwa.

2/2/26 • 21:40

Send us Fan Mail

1/28/26 • 23:35